Home Labarai Ƴan sanda sun fara bincike kan mutum 6 da aka yiwa yankan...

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutum 6 da aka yiwa yankan rago a Jihar

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta ce ta fara bincike kan wani mummunan kisa da ya auku a unguwar Dorayi Chiranchi dake jihar Kano a ranar asabar.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu da ba a san ko su wane ba sun shiga gidan Haruna Bashir, inda suka kai hari kan Fatima Abubakar mai shekaru 35 da ’ya’yanta shida, lamarin da ya yi sanadin rasuwarsu.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa lamarin ya faru ne inda maharan suka shiga gidan ba tare da an gano su ba, suka aikata wannan ta’asa kafin su tsere daga wurin.
Maƙwabta sun ce sun farga ne da jin ihun mutane da kukan neman taimako, amma kafin a kai dauki, an riga an yi mummunan lahani.

Waɗanda abin ya rutsa da su sun haɗa da Fatima Kabir, matar gidan mai kimanin shekaru 35, sai babbar ‘yarta Maimuna Haruna da ƙanwarta. Aisha Haruna da ƙannenta maza Bashir da Abubakar, sai kuma jariri wanda ake goyo wanda aka jefa shi a rijiya bayan an kashe shi.

Jami’an tsaro sun isa wurin bayan samun rahoton faruwar lamarin, inda suka killace yankin domin fara bincike.

An kuma kwashe gawarwakin mamatan zuwa asibiti domin tantancewa da kuma shirya musu jana’iza kamar yadda addinin musulunci ya tanada.

Al’ummar yankin sun nuna matuƙar alhini da damuwa kan wannan lamari, inda da dama ke kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara tsaurara matakan tsaro, domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Hukumar ’yan sanda ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ta fara bincike mai zurfi domin gano waɗanda suka aikata laifin.

Ta kuma yi kira ga jama’a da su bayar da duk wani bayani da zai taimaka wajen cafke masu hannu a wannan aika-aika.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wanda aka kama, yayin da bincike ke ci gaba. Al’umma na ci gaba da nuna alhini da jimami, tare da addu’a ga mamatan da kuma fatan ganin adalci ya tabbata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp