Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa sama da ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a wannan shekara, saboda rage tallafin da ake bayar wa a duniya.
Read Also:
MDD ta ce kusan yara miliyan uku na barazanar rasa abinci mai gina jiki, inda tuni ake cikin mawuyacin hali a jihohin Borno, Yobe da kuma Adamawa waɗanda rikici ya ɗaiɗaita.
Kodinetan hukumar ba da agaji na MDD a Najeriya, ya ce yanzu ba za a iya dogaro da agajin da aka saba bayar wa ba.
Hukumar ta ce yanzu za ta mayar da hankali ne kawai kan ayyukan ceton rai, inda za ta samar da kusan dala 500,000 don taimakawa mutane miliyan biyu da rabi.










