Home Labarai rahotannin daga jihar Katsina na cewa ‘Yan bindiga sun kashe mutum 9...

rahotannin daga jihar Katsina na cewa ‘Yan bindiga sun kashe mutum 9 a jihar

Ana ci gaba da zaman ɗar-ɗar a garuruwan Kauran Fawa da Unguwar Jika, da wasu garuruwa a ƙaramar hukumar Ɗan Ɗume a Jihar Katsina, bayan wani hari da wasu ’yan bindiga suka kai inda ake fargabar sun kashe mutum tara, tare da jikkata wasu 13.

Harin wanda aka kai cikin daren Alhamis na zuwa ne duk da sulhun da masu ruwa da tsaki a yankin suka jagoranta da ’yan bindigar, a wani yunƙuri na dawo da zaman lafiya da kare rayuka da kuma dukiyoyin al’umma.

Sai dai, hukumomin yankin sun ce sun halarci jana’izar mutum biyar, kuma suna ci gaba da ɗaukar matakai domin dawo da zaman lafiya.

Wani mazaunin ɗaya daga cikin garuruwan da abin ya shafa, wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya shaida wa manema labarai cewa ƴanbindigar sun shiga garin ne a ƙafa inda suka yi ta harbi.

“Mutum tara ne suka mutu sakamakon harbin da yanbindigar suka yi, sannan 13 ne suka samu raunuka inda muka kai su asibiti domin samun kulawa. Sun ɗauki mutum aƙalla goma amma sai suka yi ta sakin mutanen sakamakon artabu. Mutum ɗaya ne ya rage a hannun su,” in ji shi.

Shugaban karamar hukumar Ɗan Dume, Bishir Hadi, ya tabbatar da afkuwar lamarin, inda ya ce tare da shi aka yi jana’izar mutanen da aka kashe.

“Mun yi sulhu kuma mun samu nasara, tsawon wata biyar ba a kawo hari ba sai yanzu. Kafin yanzu babu ranar da ba a kawo mana hari,” in ji Bishir.

Jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya ta daɗe tana fama da hare-haren ’yan bindiga.

Duk da sulhun da gwamnatin jihar ta yi da ƴanbindigar tare da sakin wasu da aka kama, amma hukumomin na cewa matakin na daga cikin yarjejeniyoyin da wasu al’ummomin jihar suka amince da su domin samun zaman lafiya mai ɗorewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp