karo na biyu a shekarar 2026 Babban layin wutar lantarkin Najeriya ya sake lalacewa

Najeriya ta sake fuskantar katsewar wutar lantarki sakamakon lalacewar babban layin lantarkin ƙasar a ranar Talata,

Wannan shi ne karo na biyu da babban layin wutar ke fuskantar irin wannan matsala a shekarar 2026 wanda ya haifar da katsewar wutar lantarki a fannoni da dama na ƙasar.

Layin wutar ya fara lalacewa ne a ranar Juma’a da ta gabata.

Masana da hukumomi sun danganta lalacewar da tangarɗar na’ura da rashin cikakken gyare-gyare da kulawa ga manyan layukan wuta.

Bincike ya nuna cewa dukkanin tashoshin samar da wutar lantarki 23 da ke haɗe da babban layin sun daina aiki gaba ɗaya.

A halin yanzu, babu cikakken bayani kan abin da ya janyo wannan lalacewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com