Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na operation enduring peace sun lalata wata maɓoyar masu garkuwa da mutane tare da ceto mutum takwas a dajin Badurum Kasa da ke ƙaramar hukumar Kauru a jihar Kaduna

Rundunar ta ce sojojin sun samu wannan nasarar ne a yayin wani samame da suka kai a wurin maɓoyar.

Samamen ya gudana ne a ranar 28 ga Janairun 2026, bayan samun sahihin bayanan sirri kan inda masu laifin ke ɓoye.

A cewar sanarwar da rundunar ta fitar, sojojin sun kai samamennne cikin gaggawa tare da haɗin gwiwar rundunar ƴansandan Zango Kataf da dakarun sa kai ta CJTF da masu gadin daji da kuma mafarauta inda suka kutsa cikin dajin domin kama masu garkuwar.

Sojojin sun yi arangama da masu garkuwa da mutanen inda wasu suka tsere suka bar waɗanda suka sace a baya lamarin da ya sa sojojin suka yi nasarar ceto mutane takwas.

An haɗa mutanen da aka ceto su da iyalansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com