Home General Kotu ta hana ƙungiyoyin ƙwadago yin yajin aiki ko zanga-zanga

Kotu ta hana ƙungiyoyin ƙwadago yin yajin aiki ko zanga-zanga

Kotun warware matsalolin ma’aikata ta ƙasa ta bayar da umarnin wucin-gadi da ke hana manyan ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya, ciki har da NLC da TUC, tare da wasu ƙungiyoyi uku, yin yajin aiki ko zanga-zangar da suka shirya farawa.

Mai shari’a Emmanuel Subilim ne ya bayar da umarnin a birnin Abuja, bayan sauraron buƙatar gaggawa da Ministan Babban Birnin Tarayya, Abuja, Nyesom Wike, tare da hukumar ma’aikatan babban birnin tarayya FCTA suka shigar.

Alƙalin ya umurci waɗanda ake ƙara, tare da wakilansu ko jami’ansu, da su dakatar da duk wani nau’i na yajin aiki ko zanga-zanga har zuwa lokacin da za a saurari buƙatar da aka gabatar.

Haka kuma, kotun ta umurci hukumomin tsaro da ke cikin ƙarar da su tabbatar da cewa an kiyaye doka da oda, tare da hana duk wani rikici a Babban Birnin Tarayya.

Lauyan da ke wakiltar minista Wike da FCTA, Ogwu Onoja, ya shaida wa kotu cewa shugaban ƙungiyar ƙadago ya fitar da wata sanarwar tattara mambobi da ƙungiyoyin haɗin gwiwa domin shirya babbar zanga-zanga a ranar 3 ga Fabrairu, lamarin da ya ce ya saɓa wa umarnin kotu.

Sanarwar, wadda shugabannin ƙungiyoyin biyu suka rattaɓa wa hannu, ta umurci ma’aikatan da ke yajin aiki da su ci gaba, bisa hujjar cewa lauyansu, Femi Falana, ya shigar da ƙara zuwa kotun ɗaukaka ƙara kan hukuncin wucin-gadin da kotu ta yanke.

Haka kuma, an ce haɗakar ƙungiyar ƴan ƙwadago ta JUAC ta fitar da wata sanarwa da ke umartar dukkan ma’aikata da su ci gaba da yajin aikin, matakin da ɓangaren masu ƙara suka ce na iya haddasa rushewar doka da oda a Babban Birnin Ƙasa.

Kotun ta ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 10 ga Fabrairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp