Home Labarai Amurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da...

Amurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- Trump

Donald trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa zai iya sake ƙaddamar da hare-hare a Najeriya matuƙar bai gamsu da ƙoƙarin ƙasar ba wajen daƙile hare-hare a kan kiristoci.

Trump ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a lokaci da yake jawabi a ranar addu’a ta ƙasar Amurka karo na 74, wadda aka yi a birnin Washington.

“Duk wanda ya kai wa kiristoci hari, ya san dole Trump zai mayar da martani mai zafi. Na san maganar babu daɗi, amma ita ce magaar gaskiya,” in ji shi.

A lokacin taron addu’ar, Trump ya bayyana zuwan uwargidan Shugaban Najeriya, Remi Tinubu a addu’ar, inda ya yaba mata, sannan ya ce mata ce mai mutunci da ƙima.

Trump na bayani ne kan zargin da ake yi cewa ana yi wa kiristoci kisan kiyashi a Najeriya, lamarin da Amurka ta sa baki, har ta ƙaddamar da hare-hare a ƙasar a bara.

Sai dai Najeriya ta sha nanata cewa kashe-kashen da ake yi a ƙasar ba su da alaƙa da bambancin addini ko ƙabilanci, sannan ta ƙara da cewa tana ƙoƙarinta na magance matsalar.

Trump ya ce hare-haren da ya kai a Najeriya, ya yi ne tare da haɗin gwiwar hukumomin Najeriya, inda ya ce ya amince a kai harin ne domin fatattakar mayaƙan IS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp