Home Labarai Majalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓe

Majalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓe

Majalisar Dattawan Najeriya ta kafa kwamtin da za su yi nazari kan gyaran dokar zaɓe inda da naɗa mambobi 12 da za su yi aiki tare da Majalisar Wakilai.

Wannan mataki ya zo ne a lokacin da majalisar ke fuskantar ƙarin matsin lamba kan amincewa da wajabcin tura sakamakon zaɓe ta na’ura kai tsaye daga rumfunan kaɗa ƙuri’a yadda mutane za su iya gani.

Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio ya bayyana cewa an naɗa wadannan mambobi ne domin samar da kyakkyawar fahimta tsakanin majalisun biyu, da kuma tabbatar da cewa duk wani gyara da za a yi zai amfanar da dimokuradiyya a ƙasar.

Ana sa ran waɗannan mambobi za su tattauna kan dukkan abubuwan da suka janyo ce-ce-ku-ce, musamman yadda za a tabbatar da gaskiya da sahihancin sakamakon zabe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp