Home Labarai Sojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a Borno

Sojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun daƙile wani hari da mayaƙan ISWAP suka kai kan sansanin sojin Auno a Borno, sannan suka kaddamar da harin ramuwar gayya wacce ta lalata kayan yaƙi da dabarun ‘yan ta’addan.

Rundunar ce ta sanar da hakan a wata sanarwa da ta fitar wa manema labarai.

Sanarwar ta ce “A daren 5 ga Fabrairun 2026, mayaƙan ISWAP sun kai hari kan wani sansanin sojoji amma Sojojin sun dakile harin cikin tsari da ƙwarewa.”

Bayan daƙile harin, a ranar 9 ga Fabrairu, sojojin tare da hadin gwiwar dakarun sa kai ta CJTF suka ƙaddamar da samame ta ramuwar gayya a kan mayaƙan ISWAP ɗin a layin Komala da ke ƙaramar hukumar Konduga.

A yayin samamen, sojojin sun kashe mayaƙan Iswap 16, yayin da sauran suka tsere da raunuka masu tsanani.

Haka kuma, sojojin sun ƙwato fiye da kekuna 20 da kayayyakin yaƙi da dama da makamai da sauran kayan amfani na ‘yan ta’adda.

Sojojin sun kuma kama wasu mutane da ake zargin suna tura ƙwayoyi da sauran kayan aiki don taimakawa ayyukan ISWAP a yankin Bukarti.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp