Home Labarai Sojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a Borno

Sojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun daƙile wani hari da mayaƙan ISWAP suka kai kan sansanin sojin Auno a Borno, sannan suka kaddamar da harin ramuwar gayya wacce ta lalata kayan yaƙi da dabarun ‘yan ta’addan.

Rundunar ce ta sanar da hakan a wata sanarwa da ta fitar wa manema labarai.

Sanarwar ta ce “A daren 5 ga Fabrairun 2026, mayaƙan ISWAP sun kai hari kan wani sansanin sojoji amma Sojojin sun dakile harin cikin tsari da ƙwarewa.”

Bayan daƙile harin, a ranar 9 ga Fabrairu, sojojin tare da hadin gwiwar dakarun sa kai ta CJTF suka ƙaddamar da samame ta ramuwar gayya a kan mayaƙan ISWAP ɗin a layin Komala da ke ƙaramar hukumar Konduga.

A yayin samamen, sojojin sun kashe mayaƙan Iswap 16, yayin da sauran suka tsere da raunuka masu tsanani.

Haka kuma, sojojin sun ƙwato fiye da kekuna 20 da kayayyakin yaƙi da dama da makamai da sauran kayan amfani na ‘yan ta’adda.

Sojojin sun kuma kama wasu mutane da ake zargin suna tura ƙwayoyi da sauran kayan aiki don taimakawa ayyukan ISWAP a yankin Bukarti.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp