Home Labarai Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta Kwankwaso

Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta Kwankwaso

Ƙungiyar Kwankwasiyya a jihar Kano ta mayar da martani kan ƙudurin da wasu mambobin majalisar wakilan Amurka suka gabatar na a hukunta jagoranta Musa Kwankwaso dangane da zargin musguna wa Kiristoci a Najeriya.

A cikin wata sanarwar da ta fitar, ƙungiyar ta ce “duk da cewa tana sane da muhimmancin damuwar ƙasashen duniya kan batutuwan haƙƙin dan’adam da ‘yancin addini, amma kuma Najeriya ta kasance ƙasa mai yalwar al’adu da addinai, kuma tana fuskantar matsalolin tsaro masu sarƙaƙiya da ke shafar kowane ɓangare ba tare da bambancin addini ko ƙabila ba.”

A ranar Laraba ne wasu ‘yan majalisar wakilan Amurka suka gabatar da ƙuduri a zauren majalisar suna bukatar a sanya takunkumi kan Kwankwaso da wasu kungiyoyi da suka kira na “‘yan bindiga” wadanda suka zarga da taimakawa wajen cusguna wa mabiya addinin Kirista a kasar.

Sai dai kungiyar ta Kwankwasiyya ta bayyana Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu fafutukar tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan kasa.

Ta ce “yana da goyon bayan al’ummomin addinai daban daban, kuma a kullum yana inganta juriya da fahimtar juna tsakanin mabambantan ɓangarori.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp