Home Labarai Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta Kwankwaso

Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta Kwankwaso

Ƙungiyar Kwankwasiyya a jihar Kano ta mayar da martani kan ƙudurin da wasu mambobin majalisar wakilan Amurka suka gabatar na a hukunta jagoranta Musa Kwankwaso dangane da zargin musguna wa Kiristoci a Najeriya.

A cikin wata sanarwar da ta fitar, ƙungiyar ta ce “duk da cewa tana sane da muhimmancin damuwar ƙasashen duniya kan batutuwan haƙƙin dan’adam da ‘yancin addini, amma kuma Najeriya ta kasance ƙasa mai yalwar al’adu da addinai, kuma tana fuskantar matsalolin tsaro masu sarƙaƙiya da ke shafar kowane ɓangare ba tare da bambancin addini ko ƙabila ba.”

A ranar Laraba ne wasu ‘yan majalisar wakilan Amurka suka gabatar da ƙuduri a zauren majalisar suna bukatar a sanya takunkumi kan Kwankwaso da wasu kungiyoyi da suka kira na “‘yan bindiga” wadanda suka zarga da taimakawa wajen cusguna wa mabiya addinin Kirista a kasar.

Sai dai kungiyar ta Kwankwasiyya ta bayyana Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu fafutukar tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan kasa.

Ta ce “yana da goyon bayan al’ummomin addinai daban daban, kuma a kullum yana inganta juriya da fahimtar juna tsakanin mabambantan ɓangarori.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp