Home Labarai Gwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin...

Gwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8

Gwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin kuɗi naira biliyan 5 domin rage raɗaɗin mummunar gobarar da ta ƙone kasuwar bayan wata gobara da ta tashi a cikin kasuwar.

Mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima ne ya jagoranci wata tawaga zuwa jihar Kano wadda shugaban ƙasa Bola Tinubu ya aika jihar domin jajantawa waɗanda ibtila’in gobarar ya shafa.

A lokacin da yake jawabi cikin dandazon ƴan kasuwar Kashim Shettima ya jajantawa ƴan jama’a tare da sanar da tallafin da gwamnatin tarayya ta bai wa ƴan kasuwar na Naira biliyan 5.

Shettima ya ce gwamnonin jam’iyyar APC 29 sun bada tallafin naira biliyan 3 ga wadanda suka tafka wannan asara, inda ya ce za su miƙa jimillar kuɗi naira biliyan 8 ga gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf domin a hada kwamitin da za a tallafawa ƴan kasuwar.

“Bugu da ƙari, gwamnoninmu na APC guda 29 suma sun kawo tallafin biliyan 3. A taƙaice jama’a, Insha Allah za mu damƙawa gwamnan jihar Kano naira biliyan 8, zai haɗa kwamiti”

Mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima ya ce Kano ita ce cibiyar Arewa don haka za su haɗa hannu domin ganin cewa sun ceto al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp