Home Labarai Gwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin...

Gwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8

Gwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin kuɗi naira biliyan 5 domin rage raɗaɗin mummunar gobarar da ta ƙone kasuwar bayan wata gobara da ta tashi a cikin kasuwar.

Mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima ne ya jagoranci wata tawaga zuwa jihar Kano wadda shugaban ƙasa Bola Tinubu ya aika jihar domin jajantawa waɗanda ibtila’in gobarar ya shafa.

A lokacin da yake jawabi cikin dandazon ƴan kasuwar Kashim Shettima ya jajantawa ƴan jama’a tare da sanar da tallafin da gwamnatin tarayya ta bai wa ƴan kasuwar na Naira biliyan 5.

Shettima ya ce gwamnonin jam’iyyar APC 29 sun bada tallafin naira biliyan 3 ga wadanda suka tafka wannan asara, inda ya ce za su miƙa jimillar kuɗi naira biliyan 8 ga gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf domin a hada kwamitin da za a tallafawa ƴan kasuwar.

“Bugu da ƙari, gwamnoninmu na APC guda 29 suma sun kawo tallafin biliyan 3. A taƙaice jama’a, Insha Allah za mu damƙawa gwamnan jihar Kano naira biliyan 8, zai haɗa kwamiti”

Mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima ya ce Kano ita ce cibiyar Arewa don haka za su haɗa hannu domin ganin cewa sun ceto al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp