Home Labarai Yadda Lakurawa suka kashe masallata a Kebbi

Yadda Lakurawa suka kashe masallata a Kebbi

Afghan military personnel walk near the airport during fighting between Taliban militants and Afghan security forces in Kunduz on October 1, 2015. Afghan forces pushed into the centre of Kunduz on October 1, triggering pitched gunfights as they sought to flush out Taliban insurgents who held the northern city for three days in a stinging blow to the country's NATO-trained military The stunning fall of the provincial capital, even temporarily, highlighted the stubborn insurgency's potential to expand beyond its rural strongholds in the south of the country Afghan forces, hindered by the slow arrival of reinforcements but backed by NATO special forces and US air support, struggled to regain control of the city after three days of heavy fighting. AFP PHOTO / Wakil Kohsar

Kamfanin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa aƙalla masallata biyar ne suka mutu yayin da wasu uku kuma suka jikkata a wani harin ramuwar gayya da mayaƙan Lakurawa suka kai a masallaci a jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya, a daren Laraba.

Lakurawan sun buɗe wuta a masallacin dake ƙauyen Dadin Kowa a ƙaramar hukumar Maiyama yayin da masallata ke gudanar da sallar tarawihi a wata mai tsarki ta Ramadan.

Wani rahoton tsaro da kamfanin dillancin labarai na AFP ya samu ya ce an kashe mutane goma a harin.

Kakakin ‘yan sandan Kebbi, Bashir Usman, bai amsa buƙatar AFP na ƙarin bayani ba nan take, amma ya shaida wa NAN cewa harin ya biyo bayan kashe wasu daga cikin mayakan Lakurawa a wani “yunƙurin kautan ɓauna da bai yi nasara ba a kan jirgin soji.

Usman ya ce: “Harin na ramuwar gayya ne daga wasu yanbindiga da ake zargin ƴan kungiyar Lakurawa ne, bayan wani yunƙurin kautan ɓauna da bai yi nasara ba a kan rundunar sojin Najeriya.”

An danganta Lakurawa da kai hare-hare da dama a al’ummomin arewacin jihar Kebbi da jihar Sokoto dake makwabta.

Yan kungiyar na kai hare-hare daga sansanin su a cikin daji tare da satar dabbobi da kuma tilastawa mazauna biyan haraji.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp