Adadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya – MSF
Ƙungiyar MSF wato Doctors Without Borders a Najeriya ta ce adadin masu fama da cutar tamowa na ƙaruwa a Najeriya, musamman a arewacin ƙasar.
Read Also:
MSF ta bayyana haka ne a rahoton ayyukanta na Najeriya na shekarar 2025, wanda ya bayyana irin matsalolin lafiya da na jin ƙai da ake fuskanta a faɗin ƙasar da kuma yadda ƙungiyar ta bayar da tallafi.
A shekarar 2025, MSF ta ce ta kula da yara sama da 440,000 masu fama da tamowa, ta yi wa mutane sama da 300,000 maganin zazzaɓin cizon sauro, sannan ta taimaka wajen haihuwa sama da 33,500.
Ƙungiyar ta ce fiye da ma’aikata 3,500 na MSF sun yi aiki a jihohi 10 domin kai muhimman ayyukan lafiya ga wadanda suka fi bukata











