Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina

'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina

 

’Yan bindigar daji sun kai hari a ƙauyen Kogari da ke cikin ƙaramar hukumar Matazu ta Jihar Katsina inda suka yi awon gaba da Maigari na Kogari Alhaji Bello Abdulkarim tare da ɗiyarsa.

An yi awon gaba da su ne da wasu mata biyu gami da wasu mutanen da har yanzu ba a tantance yawan su ba, an kai harin ne a daren Talatar.

Kazalika, maharan sun yi awon gaba da matar wakilin Maigarin shi ma tare da ɗiyar shi.

Harin da shaidu da ido suka ce ya jefa jama’a cikin tararrabi a ƙaramar hukumar Matazu na daga cikin ƙananan hukumomin da ake zargin ƙasurgumin ɗan ta’addan nan mai suna Muhammadu Fulani ya addaba.

Shi dai Fulani shi ne wanda ya yi watsi da sasancin da aka yi da a su a kwanakin. Har zuwa haɗa wannan rahoto babu wata hukumar tsaro da tace uffan a kai

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp