Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina

'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina

 

’Yan bindigar daji sun kai hari a ƙauyen Kogari da ke cikin ƙaramar hukumar Matazu ta Jihar Katsina inda suka yi awon gaba da Maigari na Kogari Alhaji Bello Abdulkarim tare da ɗiyarsa.

An yi awon gaba da su ne da wasu mata biyu gami da wasu mutanen da har yanzu ba a tantance yawan su ba, an kai harin ne a daren Talatar.

Kazalika, maharan sun yi awon gaba da matar wakilin Maigarin shi ma tare da ɗiyar shi.

Harin da shaidu da ido suka ce ya jefa jama’a cikin tararrabi a ƙaramar hukumar Matazu na daga cikin ƙananan hukumomin da ake zargin ƙasurgumin ɗan ta’addan nan mai suna Muhammadu Fulani ya addaba.

Shi dai Fulani shi ne wanda ya yi watsi da sasancin da aka yi da a su a kwanakin. Har zuwa haɗa wannan rahoto babu wata hukumar tsaro da tace uffan a kai

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp