Home SIYASA Farfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Farfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Isa Pantami

Farfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Tsohon ministan sadarwa na Najeriya, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya janye daga zaɓen fitar da gwani na gwamnan Gombe na jam’iyyar APC.

Cikin wani saƙo da Farfesa ya wallafa a shafukansa na sada zumunta ya ce ya ɗauki matakin ne bayan zargin jam’iyyar da karya dokar zaɓe da kuma rashin bin ƙa’idojin gudanar da zaɓen.

Farfesa Pantami ya ce ya fice daga zaɓen fitar da gwanin da ake sa ran gudanarwa ranar 21 ga Mayu “cikin nuna rashin amincewa da tsarin da aka yi”.

Ya ci gaba da cewa shugabannin jam’iyyar sun kasa yin bayani a kan yadda aka tsara zaɓen cikin aminci.

Ya ce an yi watsi da buƙatun da ya gabatar domin neman bayanai kan yadda za a tantance wakilai, da tsarin kaɗa ƙuri’a da wuraren tattara sakamako.

Pantami ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓa da magoya baya da masu ruwa da tsaki, sakamakon abin da ya kira rashin gaskiya da kura-kurai a zaɓen fitar a gwani na ‘yan takarar majalisar dokoki da APC ta gudanar a jihar kwanan nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp