Home Labarai Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

Sojoji

Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

 

Bayanai sun ce mayaƙan Lakurawa sun kai wa dakarun farmaki ne a yayin da suke ƙoƙarin gyara motar su da ta lalace a kan hanya.

Aƙalla sojojin Najeriya bakwai ne suka rasa rayukansu a wani harin kwanton ɓauna da ake zargin mayaƙa masu iƙirarin jihadi suka kai musu a Jihar Sakkwato Arewa maso Yamma.

Majiyoyin soji da na cikin gida sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a daren Asabar, lokacin da dakarun ke dawowa daga wani samame da suka kan sansanin ’yan ƙungiyar Lakurawa a garin Illela da ke iyakar Najeriya da Jamhuriyyar Nijar.

Rahotanni sun ce mayaƙan sun kai wa sojojin hari ne bayan ɗaya daga ayarin motocinsu ta lalace a kan hanya, lamarin da ya tilasta mata tsayawa yayin da sauran motoci biyun suka ci gaba da tafiya.

Wata majiya ta shaida cewa mayaƙan Lakurawa sun kai wa dakarun farmaki ne a yayin da suke ƙoƙarin gyara motar, inda suka kashe sojoji bakwai ciki har da wani mai muƙamin Laftanar.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa soja guda ɗaya ne ya tsira daga harin, yayin da sauran suka rasa rayukansu.

Rundunar Sojin Najeriya ta tabbatar da faruwar harin, sai dai ba ta bayyana adadin waɗanda suka mutu ba.

Kakakin rundunar, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya ce an tura ƙarin dakarun gaggawa zuwa yankin domin ci gaba da kai farmaki da kuma fatattakar maharan.

Ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin gano tare da murƙushe waɗanda suka kai harin.

Ƙungiyar Lakurawa, wacce ake alaƙanta ta da wasu ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi a yankin Sahel, ta ƙara ƙarfi a jihohin Kebbi da Sakkwato tun daga 2018, inda ta fara zama barazanar tsaro musamman daga shekarar 2023.

A baya, rahotanni sun nuna cewa an sha gudanar da hare-haren haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da ƙasashen waje kan sansanonin ƙungiyar a yankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp