Jami’an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji
Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (DSS) sun kama tsohon ministan kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, a safiyar ranar Laraba a filin jirgin saman Akanu Ibiam da ke Enugu.
Rahotanni sun ce an kama Nnaji ne yayin da yake shirin hawa jirgi zuwa Abuja.
Wasu majiyoyin tsaro sun ce jami’an DSS sun kama shi ne bisa buƙatar Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC, wadda ake zargin tana bincikensa kan zargin amfani da takardun bogi
Daga bisani an miƙa shi ga hukumar ICPC, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Read Also:
Majiyoyin sun kuma ce ICPC ta taɓa gayyatar tsohon ministan sau da dama bayan samun koke-koke kan yadda ya gudanar da ma’aikatar da yake jagoranta, lamarin da ya sa ta nemi taimakon DSS domin cafke shi.
Uche Nnaji ya yi murabus daga muƙaminsa a ranar 7 ga Oktoban 2025, bayan ce-ce-ku-cen da suka biyo bayan takardun karatunsa daga Jami’ar Najeriya (UNN) da kuma takardar kammala bautar ƙasa ta NYSC.
A lokacin, ya ce murabus ɗin ba yana nufin amincewa da laifin da ake zarginsa da shi ba ne, illa dai mataki ne na mutunta tsarin shari’a, inda ya ce zarge-zargen suna da alaƙa da siyasa.
A watan Nuwamban 2025, ya shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya domin tilasta wa Jami’ar da shugaban jami’ar su ba shi kwafin cikakken bayanan karatunsa.
Lamarin ya sake ɗaukar sabon salo ne bayan jam’iyyar PDP ta zaɓi Uche Nnaji a matsayin ɗan takararta na gwamnan jihar Enugu a zaɓen 2027.












