Home Labarai Jami’an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji

Jami’an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji

Jami’an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji

 

Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (DSS) sun kama tsohon ministan kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, a safiyar ranar Laraba a filin jirgin saman Akanu Ibiam da ke Enugu.

Rahotanni sun ce an kama Nnaji ne yayin da yake shirin hawa jirgi zuwa Abuja.

Wasu majiyoyin tsaro sun ce jami’an DSS sun kama shi ne bisa buƙatar Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC, wadda ake zargin tana bincikensa kan zargin amfani da takardun bogi

Daga bisani an miƙa shi ga hukumar ICPC, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Majiyoyin sun kuma ce ICPC ta taɓa gayyatar tsohon ministan sau da dama bayan samun koke-koke kan yadda ya gudanar da ma’aikatar da yake jagoranta, lamarin da ya sa ta nemi taimakon DSS domin cafke shi.

Uche Nnaji ya yi murabus daga muƙaminsa a ranar 7 ga Oktoban 2025, bayan ce-ce-ku-cen da suka biyo bayan takardun karatunsa daga Jami’ar Najeriya (UNN) da kuma takardar kammala bautar ƙasa ta NYSC.

A lokacin, ya ce murabus ɗin ba yana nufin amincewa da laifin da ake zarginsa da shi ba ne, illa dai mataki ne na mutunta tsarin shari’a, inda ya ce zarge-zargen suna da alaƙa da siyasa.

A watan Nuwamban 2025, ya shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya domin tilasta wa Jami’ar da shugaban jami’ar su ba shi kwafin cikakken bayanan karatunsa.

Lamarin ya sake ɗaukar sabon salo ne bayan jam’iyyar PDP ta zaɓi Uche Nnaji a matsayin ɗan takararta na gwamnan jihar Enugu a zaɓen 2027.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Jami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya 
X whatsapp