Home SIYASA Mutane 2 Sun Rasa Rayukansu a Zaben Deleget na PDP a Jahar...

Mutane 2 Sun Rasa Rayukansu a Zaben Deleget na PDP a Jahar Osun

Mutane 2 Sun Rasa Rayukansu a Zaben Deleget na PDP a Jahar Osun

Akalla mutum biyu sun rasa rayukansu yayinda da dama suka jikkata a zaben deleget na jam’iyyar People’s Democratic Party PDP dake gudana a jihar Osun.

Kakakin hukumar yan sandan jihar, Yemisi Opalola, ta tabbatar da hakan ga manema labarai ranar Laraba a Osogbo, TVCNews ta ra

waito. A cewarta, an kashe wani matashi mai suna Toheeb Mutallib a Oke Oba, Agberire a karamar hukumar Iwo, yayinda aka kashe wani dan jam’iyyar siyasa Aremu Olamide a Ipetumodu, karamar hukumar Ife-North.

asu masu idanuwan shaida sun bayyana cewa an yiwa mutane da dama jina-jina yayinda yan daba suka kai hari garuruwa irinsu Ede, Osogbo, Odo-Otin, Olorunda, Iwo, da sauransu.

Hakazalika an bankawa mota wuta a Ipetumodu sakamakon rikici tsakanin yan daba.

Kawo yanzu Alkalin zaben, Gwamnan jihar Adamawa, Ahmad Fintiri, basu isa wajen tattara zabe ba.

Za’a zabi mutum uku-uku a gundumomin jihar 332 kuma su zasu kada kuri’a a zaben fidda gwanin dan takaran gwamna a ranar 7 ga Maris, 2022.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp