Home SIYASA Gwamnan Jahar Ebonyi David Umahi ya ɗaukaka Kara Kan Tsige Shi Daga...

Gwamnan Jahar Ebonyi David Umahi ya ɗaukaka Kara Kan Tsige Shi Daga Mulki

Gwamnan Jahar Ebonyi David Umahi ya ɗaukaka Kara Kan Tsige Shi Daga Mulki

Gwamnan jahar Ebonyi David Umahi da ke kudu maso gabashin Najeriya ya daukaka kara game da hukuncin wata babbar kotun tarayya wadda ta bayar da umurnin sauke shi daga mulki bisa sauya sheka da ya yi daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Takardar da suka gabatar ta daukaka karar, ta ce kotun ta yi kuskure a hukuncin da ta yanke, saboda haka ne ya ce yana da ja da daukacin shari’ar.

Takardar ta ce kotun ta gaza bisa dogaron da ta yi da sashen na 68, da na 109 na kundin tsarin Mulki wanda dole gwamnan ya bar mukaminsa kasancewar ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP wadda aka zabe shi a karkashinta, zuwa jam’iyyar APC mai mulkin kasar, wanda hakan a cewar takardar tamkar watsi ne da wani hukunci da kotun kolin kasar ta taba yankewa, tsakanin ministan shari’a na Najeriya da tsohon mataimakain shugaban kasa Atiku Abubakar, inda ta ce babu wani tanadin kundin tsarin mulki da ya haramta wa shugaban kasa, ko mataimakinsa, ko kuma gwamnan, ko mataimakinsa daga sauya sheka daga wata jam’iyya zuwa wata.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp