Home SIYASA Da Fadin Cigaba a Baki Zai Kawo Cigaba, da Mun Kasance Kasa...

Da Fadin Cigaba a Baki Zai Kawo Cigaba, da Mun Kasance Kasa Mafi Cigaba a Duniya – Tinubu

Da Fadin Cigaba a Baki Zai Kawo Cigaba, da Mun Kasance Kasa Mafi Cigaba a Duniya – Tinubu

 

Jigon jam’iyyar APC, Bola Tinubu, ya bayyana cewa lokaci ya yi da ya kamata yan Najeriya su fadawa juna gaskiya.

Asiwaju Bola Tinubu, ya bayyana niyyar takarar kujeran shugaban kasa a zaben Febrairun 2023.

Tinubu ya bada kyautar cibiyar karatu na kimanin kudi biliyan daya ga jami’ar jihar Legas LASU.

Legas – Mai niyyar takarar kujerar shugaban kasa a 2023 kuma tsohon gwamnan jihar Legas, Asiwaju Bola Tinubu, ya bayyana cewa dukkanmu muka kashe Najeriya kuma mu zamu iya gyarata.

Ya bayyana hakan ne ranar Alhamis a lakcan bikin yaye daliban jami’ar jihar Legas LASU.

Ya samu wakilcin mataimakin gwamnan jihar Legas, Dr Obafemi Hamzat, rahoton Vanguard.

Yace:

“Mu daina yaudarar kawunanmu. Mun dade muna ikirarin cewa muna da arziki kuma gobe zamu ji dadi amma shekaru na taf iya kuma babu cigaba.”

“Da fadin cigaba a baki zai kawo cigaba, da mun kasance kasa mafi cigaba a duniya.”

“Amma kash, Najeriya na waje guda. Mun zama masu fitar da dukiyarmu amma mu shigo da kaya da tsada.”

“Wajibi ne mu fadawa juna gaskiya, mu fuskancesa mu gyara. Dukkan mu muka janyo kuma zamu iya zama mafita. Mu hada kai. Wajibi ne mu gyara kasar nan.”

A kan rashin aikin yin matasa, Tinubu ya ce rashin aiki da aiki babu albashin kwarai tsakanin matasa ya kai 60%, kuma wajibi ne a magance hakan.

Tinubu yace samawa matashin birane aikin yi, aikin noma, harkar gidaje, ilimi, tattalin arziki da manyan ayyuka ya kamata gwamnati ta mayar da hankali.

Tinubu ya bada kyautar cibiyar karatu na kimanin kudi biliyan daya ga makarantar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp