Home Taska Faɗawa Cikin Rijiya: Mutane 13 Sun Rasa Rayukansu Ana Tsaka da Shagalin...

Faɗawa Cikin Rijiya: Mutane 13 Sun Rasa Rayukansu Ana Tsaka da Shagalin Biki a Indiya

Captured Boko Haram spies by troops
Captured Boko Haram spies by troops

Faɗawa Cikin Rijiya: Mutane 13 Sun Rasa Rayukansu Ana Tsaka da Shagalin Biki a Indiya

Akalla mutum 13 ne suka rasa rayukansu bayan sun fada cikin wata rijiya yayin wani biki da ake yi a jihar Utter Pradesh da ke yammacin Indiya.

Yan sanda sun ce wadanda abin ya ritsa da su – duka mata ne da yara – na zaune kan murfin da aka rufe rijiyar da shi a lokacin da ya rufta saboda nauyin mutanen da ke kansa.

Lamarin ya faru ne ranar Laraba da yamma a lokacin bikin gargajiya na “haldi”, inda ‘yan uwa suke shafa wa ango da amarya ruwan kurkur a fuska a matsayin alamar samun wadata.

Wasu karin mutum biyu sun jikkata a hatsarin, wanda ya faru a gundumar Kushinagar.

Firaminista Narendra Modi ya bayyana mutuwar tasu a matsayin “mai sosa zuciya”.

Lokacin da murfin ya karye, sauran baki sun ruga don ceto mutanen, inda suka kai su wani asibiti da ke kusa. Yayin da aka sanar da mutuwar mutum 11 nan take, wasu biyu kuma sun mutu a asibit, in ji ‘yan sanda.

Babban Ministan Utter Pradesh Yogi Adityanath ya nemi shugabannin ananan hukumomi da su taimaka wa iyalan mutanen da abin ya ritsa da su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp