Home DUNIYA Kashi 80 Cikin 100 na Mutanen Afirka ba a yi Musu Allurar...

Kashi 80 Cikin 100 na Mutanen Afirka ba a yi Musu Allurar Rigakafin Corona ba – Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya

Kashi 80 Cikin 100 na Mutanen Afirka ba a yi Musu Allurar Rigakafin Corona ba – Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya

 

Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce kashi 80 cikin 100 na mutanen Afirka har yanzu ba a yi musu allurar riga-kafin corona ko da ɗaya ba.

Dr Tedros ya bayyana hakan ne a lokacin wani taro ta intanet yayin cika shekara daya da kaddamar da shirin samar da rigakafin a duniya da ake kira Covax.

Ya ce “kiyasinmu ya nuna cewa riga-kafin da za a samar za ta isa a yi wa dukkanin manya na duniya kuma har a kara yi wa mutanen da ke cikin hadarin kamuwa da cutar sosai zuwa wata uku na farkon shekaran nan”.

Covax shiri ne na tabbatar da raba daidai a tsakanin kasashen duniya wajen samar da riga-kafin corona.

Shugaban na WHO ya ce shirin ya gamu da nakasu sosai saboda abin da ya kira “kaka-gida” da kasashe suka yi a kan rigakafin da kuma yadda kamfanonin da ke samar da ita suka fi bayar da fifiko ga kasashe masu karfin arziki.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp