Home Taska Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da...

Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da ta Taimaka ta Kwashe su Daga Ukraine

Rikicin Ukraine da Rasha: ‘Yan Wasan Brazil Sun Roki Gwamnatin Kasarsu da ta Taimaka ta Kwashe su Daga Ukraine

Yan wasan Brazil da ke wasa a kungiyoyin Shakhtar Donetsk da Dynamo Kyiv sun roki gwamnatin kasarsu da ta taimaka ta kwashe su daga Ukraine.

Hakan ya biyo bayan hare-haren da Rasha ta fara kai wa Ukraine da safiyar Alhamis.

Wasu daga cikin yan wasan sun yada wani bidiyo a shafukan sada zumunta, inda suka bayyana halin da suke ciki tun bayan barkewar rikicin, da kuma bukatar hukumomin Brazil su taimaka su kwashe su tare da iyalansa daga Ukraine.

Dan wasan gaban Shakhtar Donetsk Junior Moraes ya rubuta a shafinsa na Instagram cewa ”halin da muke ciki ya yi muni. Ina so al’umma su yada wannan bidiyo har sai ya kai ga hukumonin Brazil.”

Ya kara da cewa ”an rufe kan iyakoki da bankuna, babu man fetur, kuma za a fuskanci karancin abinci da kudade a hannun jama’a.”

” Yan uwa da abokan arziki yanayin da muke ciki ya yi muni don mun makale a Kyiv muna neman mafita. Yanzu haka muna cikin wani otal ne. Ku taya mu da addu’a.” In ji Moraes.

Akwai akalla yan wasan Brazil 12 da ke wasa a kungiyar kwallon kafa ta Shakhtar, da suka hada da David Neres wanda bai dade da zuwa kungiyar ba daga Ajax da ke Holland.

Sauran yan wasan sun hada da Dodo, da Vitao, da Marlon, da Ismaily, da Vinicius Tobias, da Maycon, da Marcos Antonio, da Tete, da Alan Patrick, da Pedrinho da kuma Fernando.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp