Home SIYASA Tsohon Firaministan Mali Soumeylou Boubeye Maiga ya Mutu

Tsohon Firaministan Mali Soumeylou Boubeye Maiga ya Mutu

Tsohon Firaministan Mali Soumeylou Boubeye Maiga ya Mutu

Tsohon firaministan Mali Soumeylou Boubèye Maïga – wanda ke fuskantar shari’a saboda tuhumar da ake masa ta cin hanci da rashawa – ya mutu yana mai shekara 67 da haihuwa.

Mista Maiga ya mutu ne ranar Litinin a wani asibiti a Bamako, babban birnin kasar, kamar yadda iyalansa suka sanar.

Iyalan nasa sun ce an kama shi kuma an tsare da shi karkashin wani hali mai tayar da hankali. A watan Disamba aka kwantar da shi a asibiti.

Kamfanin dillancin labarai na Associated Press ya ce gwamnatin ƙasar ta ki amincewa da bukatarsa ta zuwa kasashen waje domin a duba lafiyarsa.

Sai dai ta mika sakonta na ta’aziyya ga iyalan tsohon firaministan, bayan ta fitar da wata sanarwa da ke cewa ya mutu ne bayan wata doguwar jinya da ya yi.

An dai kama Mista Maiga ne a watan Agustan bara kuma aka tsare shi bayan da aka tuhume shi da aikata laifukan cin hanci da rashawa kan yadda aka sayo wani jirgin sama na shugaban kasa, yayin mulkin hambararren shugaban kasar Ibrahim Boubacar Keïta.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp