Home SIYASA Tsohon Firaministan Mali Soumeylou Boubeye Maiga ya Mutu

Tsohon Firaministan Mali Soumeylou Boubeye Maiga ya Mutu

Tsohon Firaministan Mali Soumeylou Boubeye Maiga ya Mutu

Tsohon firaministan Mali Soumeylou Boubèye Maïga – wanda ke fuskantar shari’a saboda tuhumar da ake masa ta cin hanci da rashawa – ya mutu yana mai shekara 67 da haihuwa.

Mista Maiga ya mutu ne ranar Litinin a wani asibiti a Bamako, babban birnin kasar, kamar yadda iyalansa suka sanar.

Iyalan nasa sun ce an kama shi kuma an tsare da shi karkashin wani hali mai tayar da hankali. A watan Disamba aka kwantar da shi a asibiti.

Kamfanin dillancin labarai na Associated Press ya ce gwamnatin ƙasar ta ki amincewa da bukatarsa ta zuwa kasashen waje domin a duba lafiyarsa.

Sai dai ta mika sakonta na ta’aziyya ga iyalan tsohon firaministan, bayan ta fitar da wata sanarwa da ke cewa ya mutu ne bayan wata doguwar jinya da ya yi.

An dai kama Mista Maiga ne a watan Agustan bara kuma aka tsare shi bayan da aka tuhume shi da aikata laifukan cin hanci da rashawa kan yadda aka sayo wani jirgin sama na shugaban kasa, yayin mulkin hambararren shugaban kasar Ibrahim Boubacar Keïta.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp