Home Taska Jami’an Ukraine 300 ne Suka Rasa Rayukansu a Harin da Rasha ta...

Jami’an Ukraine 300 ne Suka Rasa Rayukansu a Harin da Rasha ta Kai Birnin Mariupol

Jami’an Ukraine 300 ne Suka Rasa Rayukansu a Harin da Rasha ta Kai Birnin Mariupol

Mun sami karin bayanai kan harin sama da dakarun Rasha suka kai a birnin Mariupol na kudancin Ukraine.

Kawo yanzu, ba a san yawan wadanda suka mutu daga harin ba saboda ci gaba da kai hare-hare babu kakkautawa da sojojin Rasha ke yi kan birnin.

Amma jami’an Ukraine a yanzu sun ce kimanin mutum 300 ne suka rasa rayukansu yayin wancan harin, wanda ya fada kan wani ginin gidan wasannin kwaikwayo, inda daruruwan ‘yan Ukraine ke neman mafaka.

Jami’an Ukraine na cewa Rasha ce ta kai harin, sai dai Rashar ta musanta ikirarin nasu.

Ofishin Magajin Garin Mariupol ya ce “Daga bayanan da shaidu suka sanar da mu, kimanin mutum 300 ne suka halaka a ginin Drama Theatre na Mariupol wanda ya biyo bayan hare-hare da jiragen yakin Rasha suka kai.”

Sai dai kafofin sadarwa da birnin na Mariupol sun kasance ‘yan kalilan, saboda haka ne babu yadda za a iya tantance sahihancin rahotannin da ke fitowa daga can.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp