‘Yan Bindiga Sun Tayar da Bam a Titin Jirgin Kasa na Abuja-Kaduna

‘Yan Bindiga Sun Tayar da Bam a Titin Jirgin Kasa na Abuja-Kaduna

Rahotanni sun ce wasu ƴan bindiga sun tayar da bam a titin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna da ke ɗauke da fasinja 970.

Rahotanni sun ce maharan sun yi nasarar hana jirgin tafiya, inda suka buɗe wuta.

Ɗaya daga cikin fasinjan da ke cikin jirgin ya tabbatar wa BBC da harin, inda ya ce maharan sun kwashi mutane sun tafi da su. Sannan jami’an tsaron da ke cikin jirgin sun yi musayar wuta da ƴan bindigar.

Ya ce sun kashe mutum guda. “Mun ji ƙarar harbe harbe, muna cikin tashin hankali,” in ji shi.

Wani ma’aikacin tashar jirgin a Rigasa ya shaida wa BBC cewa “jirgin ya kamata ya iso misalin ƙarfe 8:20 amma har yanzu ba labari.”

Hukumomin sufurin jiragen ƙasa ta Najeriya da hukumomin gwamnatin Kaduna ba su tabbatar da al’amarin ba.

Karin bayani na tafe….

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 34 minutes 42 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 16 minutes 7 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here