An Harbi Tsohon Mataimakin Gwamnan Zamfara, Ibrahim Wakkala a Harin Jirgin Kasar Abuja-Kaduna

An Harbi Tsohon Mataimakin Gwamnan Zamfara, Ibrahim Wakkala a Harin Jirgin Kasar Abuja-Kaduna

Tsohon mataimakin gwamnan Zamfara, Ibrahim Wakkala, na a cikin jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja da aka kaiwa hari a ranar Litinin.

Wakkala ya samu rauni ta sanadiyar harbin bindiga bayan tawagar tsaro sun ceto shi daga hannun yan bindigar da suka yi garkuwa da shi a yayin harin.

Yana a hanyarsa ta dawowa ne daga babban taron gangamin APC da aka yi a karshen mako.

Kaduna- Tsohon mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Ibrahim Wakkala, ya ji rauni daga harbin bindiga a harin ta’addanci da aka kai kan jirgin kasar Kaduna zuwa Abuja a ranar Litinin, 28 ga watan Maris.

Yan bindiga sun far ma jirgin kasan da ke dauke da daruruwan fasinjoji a tsakanin Katari da Rijana a jihar Kaduna.

Wani hadimin tsohon mataimakin gwamnan ya fada ma talbijin din Channel cewa an harbi Mista Wakkala ne wanda ke dawowa daga babban taron APC da aka yi a ranar Asabar a yayin musayar wuta tsakanin yan ta’addan da sojoji.

Ya kuma ce an kwashe shi zuwa wani asibitin sojoji da ke Kaduna domin jinya.

Kakakin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Zamfara, Yusuf Idris ya kuma tabbatar da lamarin ga gidan talbijin din.

Idris ya ce da farko yan bindiga sun sace tsohon mataimakin gwamnan a yayin harin amma sai tawagar hadin gwiwa ta DSS da sojoji suka yi nasarar ceto shi.

“Da farko sun sace shi amma sai DSS da sojoji suka ceto shi, a cikin haka ne ya ji rauni ta sanadiyar harbin bindiga a kafarsa.

“Ya daidaita sosai a yanzu, yana samun kulawar likitoci a asibitin jihar Kaduna.”

Daily Trust takuma nakalto Idris na kara cewa:

“Yana samun sauki sosai. Yana amsa kiraye-kirayen waya a gadonsa na asibiti. Na yi magana da shi kuma wasu mutane da dama ma sun yi. Babu wani abun tashin hankali.”

 

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 31 minutes 37 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 13 minutes 2 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here