• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Taska ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Birnin Tarayya Abuja
  • Taska

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Birnin Tarayya Abuja

By
Prnigeria
-
April 11, 2022
Arewa Award

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Birnin Tarayya Abuja

Wani rahoto ya bayyana yadda ‘Yan bindiga suka yiwa karamar hukumar Mulki ta Gwagwalada dake Birnin Tarayya Abuja tsinke, inda suka hallaka Shugaban Kungiyar Fulani Makiyaya ta Miyyetti Allah (MACBAN) Adamu Aliyu.

Maharan sun halaka Aliyu ne da wasu Karin mutum 4 a daura da kauyen Daku dake mazabar a ranar Alhamis.

Sakatararen Kungiyar ta MACBAN Muhammad Usman, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin a ranar lahadi, yace an yi garkuwa da mutum 3, bayan da wasu mutum suka sami raunukan harbi a jikin su inda suke karbar kulawa a Asibitin Koyarwa na Gwagwalada.

Yace lamarin ya auku ne a ranar Alhamis, da misalin karfe 5 na yamma, yayin da Shugaban kungiyar Fulani Makiyaya ta Miyatti Allah ke kan hanyarsu ta dawowa daga kasuwar Izom dake jihar Niger a cikin wata motar daukar kaya, nan ne ‘Yan bindigar suka fito daga cikin daji suka kuma bude wuta kan motar.

Yace ‘Yan bindigar sun fasa gilashin motar da shugaban kungiyar ta MACBAN da wasu fasinjoji ke ciki.

Read Also:

  • Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota
  • NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta
  • Kotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam Sanda

“Suna kan hanyar su ta dawowa daga sayar da shanu a kasuwar Izom ta jihar Niger, kilomita 1 ne rak ya rage musu su karaso kauyen Daku, nan ‘Yan bindigar suka afka musu da harbi daga daji, nan suka hallaka Shugaban Kungiyar ta MACBAN tare da wasu mutum 4” a cewar sa.

Ya kuma bayyana sunayen wadanda aka hallakar da suka hadar da Saleh, Aliyu, Muhammadu da kuma Saidu, yace tuni aka yi musu sutura kamar yadda addinin muslunci yayi tanadi.

Sai dai jaridar Daily trust ta rawaito cewa jami’an tsaro da suka hadar da Jami’an Civil Defence, ‘Yan Sanda Kwantar da Tarzoma ‘Yan Sa Kai ne suka halarci jana’izar.

Shugaban Karamar Hukumar Mulki ta Gwagwalada Alhaji Adamu Mustapha, ya tabbatarwa da wakilin mu faruwar lamarin ta wayar tarho, amma yace zai masa Karin bayani bayan ya kammala wata ganawar sirri da yake tsaka dayi a lokacin.

Duk kokarin da mukayi domin jin ta bakin kakakin rundunar ‘Yan Sandan birnin tarayya Abuja DSP Adeh Josephine, bata amsa kiran wayar ba, kuma bata biyo sakon karta kwanan da muka tura mata ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • 'yan bindiga
  • abuja
  • Adamu Aliyu
  • MACBAN
Previous articleRundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Kame ‘Yan Kungiyar Asiri Guda 32 a Jihar Anambra
Next articleAn Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo
Prnigeria

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Azumin Bara: Talge Muka Riƙa Sha a Hannun Maharan Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna

Zambar N2.2bn: EFCC ta Sake Gurfanar da ɗan Tsohon Shugaban PDP

Magance Karancin Naira: CBN ya Umarci Bankuna da su yi Aiki a Ranakun Asabar da Lahadi

Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

Hukumar NITDA ta Gabatar da Satifiket ga Matan da Suka Samu Horo Kan Fasahar Zamani

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

An Gudanar Da Bikin Arewa Stars 30 Under 30 2022, Cikin Nasara

Manomi Yayiwa Wata Mata Yankan Rago

‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

Gidauniyar Malam Inuwa Da Kokarinta Na Ilmantar Da Mutanen Karkara Da Rugage

Gidauniyar Malam Inuwa ta Ɗauki Nauyin Koyar da Ƴa’yan Fulani Al-ƙur’ani

Bincike: Shin Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) ta ƙirƙiro da Tambayoyi Domin Tantance kungiyoyin Musulmi da Kirista a kidayar 2023? 

Recent Posts

  • Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota
  • NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta
  • Kotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam Sanda
  • Kotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yari
  • Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1642 days 3 hours 54 minutes 52 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1624 days 5 hours 36 minutes 17 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin MotaNNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar DeltaKotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam SandaKotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yariHar yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso - TuggaNajeriya ta ce jirgin ta ya yi saukar gaggawa ne a Burkina FasoBurkina Faso ta tsare jirgin sojin Najeriya kan keta sararin samaniyar ƙasarKwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin NijeriyaAn ceto wasu daga cikin daliban da aka sace a makarantar Papiri da ke jihar NejaAmnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi MagajiAkwai sa hannun 'yan siyasa a kamen da aka yiwa Muhuyi - Gwamnatin KanoMajalisa ta amince da naɗin Chris Musa ministan tsaron NajeriyaWadanda aka sace a Cocin jihar Kwara sun shaki iskar 'yanciGwamnatin Nasarawa za ta kafa ƴan sandan JihaGwamnan Osun Ademola Adeleke ya fice daga jam’iyyar PDP
X whatsapp