• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Taska ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Birnin Tarayya Abuja
  • Taska

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Birnin Tarayya Abuja

By
Prnigeria
-
April 11, 2022
Arewa Award

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Birnin Tarayya Abuja

Wani rahoto ya bayyana yadda ‘Yan bindiga suka yiwa karamar hukumar Mulki ta Gwagwalada dake Birnin Tarayya Abuja tsinke, inda suka hallaka Shugaban Kungiyar Fulani Makiyaya ta Miyyetti Allah (MACBAN) Adamu Aliyu.

Maharan sun halaka Aliyu ne da wasu Karin mutum 4 a daura da kauyen Daku dake mazabar a ranar Alhamis.

Sakatararen Kungiyar ta MACBAN Muhammad Usman, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin a ranar lahadi, yace an yi garkuwa da mutum 3, bayan da wasu mutum suka sami raunukan harbi a jikin su inda suke karbar kulawa a Asibitin Koyarwa na Gwagwalada.

Yace lamarin ya auku ne a ranar Alhamis, da misalin karfe 5 na yamma, yayin da Shugaban kungiyar Fulani Makiyaya ta Miyatti Allah ke kan hanyarsu ta dawowa daga kasuwar Izom dake jihar Niger a cikin wata motar daukar kaya, nan ne ‘Yan bindigar suka fito daga cikin daji suka kuma bude wuta kan motar.

Yace ‘Yan bindigar sun fasa gilashin motar da shugaban kungiyar ta MACBAN da wasu fasinjoji ke ciki.

Read Also:

  • Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna
  • Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi
  • An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

“Suna kan hanyar su ta dawowa daga sayar da shanu a kasuwar Izom ta jihar Niger, kilomita 1 ne rak ya rage musu su karaso kauyen Daku, nan ‘Yan bindigar suka afka musu da harbi daga daji, nan suka hallaka Shugaban Kungiyar ta MACBAN tare da wasu mutum 4” a cewar sa.

Ya kuma bayyana sunayen wadanda aka hallakar da suka hadar da Saleh, Aliyu, Muhammadu da kuma Saidu, yace tuni aka yi musu sutura kamar yadda addinin muslunci yayi tanadi.

Sai dai jaridar Daily trust ta rawaito cewa jami’an tsaro da suka hadar da Jami’an Civil Defence, ‘Yan Sanda Kwantar da Tarzoma ‘Yan Sa Kai ne suka halarci jana’izar.

Shugaban Karamar Hukumar Mulki ta Gwagwalada Alhaji Adamu Mustapha, ya tabbatarwa da wakilin mu faruwar lamarin ta wayar tarho, amma yace zai masa Karin bayani bayan ya kammala wata ganawar sirri da yake tsaka dayi a lokacin.

Duk kokarin da mukayi domin jin ta bakin kakakin rundunar ‘Yan Sandan birnin tarayya Abuja DSP Adeh Josephine, bata amsa kiran wayar ba, kuma bata biyo sakon karta kwanan da muka tura mata ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • 'yan bindiga
  • abuja
  • Adamu Aliyu
  • MACBAN
Previous articleRundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta Kame ‘Yan Kungiyar Asiri Guda 32 a Jihar Anambra
Next articleAn Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo
Prnigeria

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Azumin Bara: Talge Muka Riƙa Sha a Hannun Maharan Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna

Zambar N2.2bn: EFCC ta Sake Gurfanar da ɗan Tsohon Shugaban PDP

Magance Karancin Naira: CBN ya Umarci Bankuna da su yi Aiki a Ranakun Asabar da Lahadi

Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

Hukumar NITDA ta Gabatar da Satifiket ga Matan da Suka Samu Horo Kan Fasahar Zamani

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

An Gudanar Da Bikin Arewa Stars 30 Under 30 2022, Cikin Nasara

Manomi Yayiwa Wata Mata Yankan Rago

‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

Gidauniyar Malam Inuwa Da Kokarinta Na Ilmantar Da Mutanen Karkara Da Rugage

Gidauniyar Malam Inuwa ta Ɗauki Nauyin Koyar da Ƴa’yan Fulani Al-ƙur’ani

Bincike: Shin Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) ta ƙirƙiro da Tambayoyi Domin Tantance kungiyoyin Musulmi da Kirista a kidayar 2023? 

Recent Posts

  • Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna
  • Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi
  • An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar
  • Turkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar Tsaro
  • Najeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasar

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1687 days 12 hours 23 minutes 0 second,



Baptist School Students, Kaduna
1669 days 14 hours 4 minutes 25 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a KadunaBa a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya - Sanata NingiAn ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin NijarTurkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar TsaroNajeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasarkaro na biyu a shekarar 2026 Babban layin wutar lantarkin Najeriya ya sake lalacewaMatatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban baraAna tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano - GwamnatiJOHESU - Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma'aikatan asibitiGwamnan Kano zai koma Jam'iyyar APCGwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan SiyasaJam’iyyar NNPP ya yi martani kan fitar Gwamnan Kano daga NNPPGwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya fice daga Jam'iyyar NNPPAmurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare Kiristoci
X whatsapp