Home WASANNI NPFL: Kungiyar Kano Pillars zata Dawo Buga Wasa Jihar Kano

NPFL: Kungiyar Kano Pillars zata Dawo Buga Wasa Jihar Kano

Hukumar kula da gasar firimiya ta Najeriya, Nigeria Professional Football League (NPFL), ta bai wa ƙungiyar ƙwallon kafa ta Kano Pillars damar ci gaba da buga wasanni a filin wasa na Sani Abacha da ke jihar Kano.

Wannan dai na cikin Wata sanarwa da hukumar ta aike wa kungiyar ta kano Pillars, inda  ta ce yanzu haka kungiyar nada damar buga wasannin a filin bayan duba na tsanaki da hukumar tayi.

Ta cikin sanarwar Hukumar ta ce wajibi ne kungiyar ta kano Pillars ta tanadi wani filin wasan da za ta ci gaba da buga wasanni da zarar an fara aikin gyara ciyawar filin taka leda ta filin kafin kammala shi.

Tuni kungiyar kwallon kafar ta kano Pillars ta amince da sharaɗin, har, inda tace za ta buga wasanta na gaba tare da kungiyar kwallon kafa ta Katsina United a Kano ranar 16 ga watan Afrilu.

Idan dai za’a iya tunawa kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ba ta buga wasa a gida ba a kakar bana sakamakon matakin da hukumar ta NPFL ta ɗauka, inda ta umarci a sauya ciyawar filin taka ledar.

Yanzu haka dai kungiyar ta Pillars na mataki na 13 da maki 26 bayan buga wasa 22 a kakar bana ta 2022/2023.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp