NPFL: Kungiyar Kano Pillars zata Dawo Buga Wasa Jihar Kano

Hukumar kula da gasar firimiya ta Najeriya, Nigeria Professional Football League (NPFL), ta bai wa ƙungiyar ƙwallon kafa ta Kano Pillars damar ci gaba da buga wasanni a filin wasa na Sani Abacha da ke jihar Kano.

Wannan dai na cikin Wata sanarwa da hukumar ta aike wa kungiyar ta kano Pillars, inda  ta ce yanzu haka kungiyar nada damar buga wasannin a filin bayan duba na tsanaki da hukumar tayi.

Ta cikin sanarwar Hukumar ta ce wajibi ne kungiyar ta kano Pillars ta tanadi wani filin wasan da za ta ci gaba da buga wasanni da zarar an fara aikin gyara ciyawar filin taka leda ta filin kafin kammala shi.

Tuni kungiyar kwallon kafar ta kano Pillars ta amince da sharaɗin, har, inda tace za ta buga wasanta na gaba tare da kungiyar kwallon kafa ta Katsina United a Kano ranar 16 ga watan Afrilu.

Idan dai za’a iya tunawa kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ba ta buga wasa a gida ba a kakar bana sakamakon matakin da hukumar ta NPFL ta ɗauka, inda ta umarci a sauya ciyawar filin taka ledar.

Yanzu haka dai kungiyar ta Pillars na mataki na 13 da maki 26 bayan buga wasa 22 a kakar bana ta 2022/2023.

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 23 minutes 3 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 4 minutes 28 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com