Home Taska Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

Tallafin Marayu

Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

 

A ƙoƙarin da ta ke kan cigaba da yi wajen ganin ta kyautatawa marayu a Jihar Jigawa a wannan wata na Ramadan mai albarka, Gidauniyar Malam Inuwa wacce mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE) ya assasa, ta rabawa marayu mata (100) tallafin turmin Atamfa domin hidimar sallah a ƙaramar hukumar Haɗejia da ke Jihar Jigawa.

Rabon wanda aka gudanar a yammacin wannan rana, a ofishin gidauniyar da ke kan titin Garun-Gabas, Haɗejia, ya gudana ne a ƙarƙashin jagorancin shugabannin gidauniyar, da kwamitin marayu na ƙaramar hukumar waɗanda su ka zaƙulo marayun da su ka fi buƙatar temako a mazaɓun yankin gabaɗaya.

Marayun da su ka halarci wurin rabon su ka karɓa, da kuma wakilan marayun waɗanda su ka karɓa musu, gabaɗaya sun bayyana godiya da farin cikinsu tare da addu’ar fatan alkhairi ga mai girma shugaban hukumar ta (NITDA), Malam Kashif gami da fatan Allah Ya ji ƙan mahaifin nasa, Malam Inuwa Ya ƙara arziƙi.

Talata, 19 ga watan Afrelu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp