Home Taska Ministan Sadarwa ya Jagoranci Bikin Tunawa da Ranar Ƙere-Ƙere ta Duniya

Ministan Sadarwa ya Jagoranci Bikin Tunawa da Ranar Ƙere-Ƙere ta Duniya

Kashifu fo

Ministan Sadarwa ya Jagoranci Bikin Tunawa da Ranar Ƙere-Ƙere ta Duniya

Mai girma ministan sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), ya jagoranci bikin tunawa da zagayowar ranar nazari da ƙirƙira ta Duniya wanda hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa, CCIE ta shirya.

Bikin na bana wanda aka yi wa take da: Nazari da ƙirƙira na matsayin bunƙasa haɗin gwiwa domin ɗorewar tattalin arziƙin zamani”, an gudanar da shi ne a cibiyar ƙere-ƙeren kayayyakin fasahar zamani ta ƙasa (NCAIR) wacce hukumar ta (NITDA) ta samar a Abuja.

Ranar Nazari da Ƙirƙira ta Duniya rana ce da aka ware domin wayar da kai gami da zaburar da al’umma muhimmancin ƙirƙiro da abubuwa na fasahar zamani waɗanda za su zama mafita kan wata matsala a fannoni daban-daban na rayuwar jama’a daida da tanadin shirin muradi mai ɗorewa na majalisar ɗinkin duniya (UN).

A bikin na bana da ya gudana a wannan rana, mai girma shugaban hukumar ta (NITDA), ya wakilci mai girma ministan na sadarwa wajen miƙa lambobin yabo da kyaututtukan kuɗi ga gwarazan da su ka yi nasarar lashe gasar ƙere-ƙeren inda na ɗaya ya samu kyautar Naira Miliyan Biyu, na biyu ya samu kyautar Naira Miliyan Ɗaya da Dubu Ɗari Biyar, Na Uku Naira Miliyan Ɗaya, sai na Huɗu ya samu kyautar Naira Dubu Ɗari Biyar, kamar yadda aka wallafa a shafin hukumar ta (NITDA) a wannan rana.

Alhamis, 21 ga watan Afrelu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp