Home Taska Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Kashifu pantami

Lambobin Yabo ga Shugaban NITDA

Hoto Na Farko:- Ƙungiyar Injiniyoyin lantarki, Institute of Electrical and Electronic Engineers (IEEE), ne su ka karrama mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da lambar yabo, yau a wurin taronsu na shekara-shekara karo na huɗu domin yabawa haɗi da jinjina kan gudunmawar da ya ke ba su.

Mai girma ministan sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, Shaik, Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), da ya miƙa masa lambar yabon, ya kasance babban baƙo mai gabatar da jawabi a wurin taron a bana, (2022).

Hoto Na Biyu: Ƙungiyar Jakadun jam’iyyar (APC), dangane da shugabanci nagari, “APC Ambassadors for Good Governance”, ita ce ta karrama mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da lambar yabo ta jinjina a gare shi akan ƙoƙarin da ya ke yi wajen cimma buri da manufofin gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari (GCFR), kan tattalin arziƙin zamani.

Shugaban riƙo na sashen tsare-tsare na hukumar ta (NITDA), Dakta Aristotle Onumo, shi ne ya karɓi lambar yabon a madadinsa, jiya, a wurin babban taron ƙungiyar na ƙaddamarwa da rantsar da shugabanninta na Jihohi (36).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp