Home Taska Hukumar NITDA ta Kammala ba da Horon Kwarewa ga Jami’an Gwamnati

Hukumar NITDA ta Kammala ba da Horon Kwarewa ga Jami’an Gwamnati

Certificate

Hukumar NITDA ta Kammala ba da Horon Kwarewa ga Jami’an Gwamnati

A ƙoƙarin da ta ke cigaba da yi wajen horar da ƴan ƙasa, gami da bunƙasa ilimin jami’an gwamnatin tarayya kan amfani da fasahar zamani, hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da ke ƙarƙashin kulawar ma’aikatar sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), ta kammala ba da horon bunƙasa ƙwarewa kan amfani da fasahar zamani ga jami’an gwamnatin tarayya.

Jami’an gwamnatin waɗanda su ka fito daga hukumomin tsaro da sauran sassan ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya, an ba su horon ƙwarewar akan harkokin tsaro na yanar gizo-gizo da sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa.

Jim kaɗan da kammala horon a wannan rana, mai girma shugaban hukumar ta (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE) wanda Dakta Usman Gambo Abdullahi, shugaban sashen warware matsalolin ayyukan fasahar zamani na hukumar ya wakilta, ya miƙawa waɗanda aka horar ɗin takardunsu na shaidar samun horon, a cibiyar horar da ma’aikata da ke yankin Kubwa a birnin tarayya, Abuja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp