Home DUNIYA An yi Musayar Fursunoni Tsakanin Rasha da Ukraine

An yi Musayar Fursunoni Tsakanin Rasha da Ukraine

Gwamnatin Ukraine ta sanar da yin musayar fursunoni sama da 100 tsakaninta da Rasha, musayar da ta ce ita ce ta farko da ta kunshi mata zalla, bayan shafe kusan watanni takwas suna gwabza yaki.

Shugaban ma’aikatar fadar shugaban Ukraine Andriy Yermak ya ce mata 108 suka samu nasarar kubutarwa yayin musayar fursunonin da suka yi da Rasha.

Yermak ya ce wasu daga cikin mutanen da aka yi musayar karbarsu daga hannun sojojin Rasha, iyaye ne da ‘yayansu mata da aka tsare su tare, yayin kawanyar da dakarun mamaya suka yi wa kamfanin sarrafa karafa na Azovstal da ke birnin Mariupol.

A cikin jawabinsa na yau da kullun da yammacin ranar Litinin, shugaba Vlodymyr Zelensky ya ce 96 daga cikin fursunonin da aka yi musanya sojoji ne mata, 12 kuma fararen hula.

Ita kuwa ma’aikatar tsaron Rasha ta ce mutanenta 72 da suka dawo daga Ukraine ma’aikatan wani jirgin ruwa ne na fararen hula da Ukraine ta tsare su tun a watan Fabrairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp