Home General Wasu ‘yan bindiga a jihar Imo sun sare kan wani shugaban...

Wasu ‘yan bindiga a jihar Imo sun sare kan wani shugaban ƙaramar hukumar Ideato ta arewa a jihar

Wasu ‘yan bindiga a jihar Imo da ke kudu maso gabashin Najeriya sun sare kan wani shugaban ƙaramar hukumar Ideato ta arewa a jihar, bayan da suka sace shi a ranar Juma’ar da ta gabata.

‘Yan bindigar dai sun saki wasu hotunan bidiyo da ke nuna yadda suka ɗaure shugaban ƙaramar hukumar a hannaye, da kuma yadda suka halaka shi, bayan sun karɓi kuɗin fansa don su sako shi.

Wata majiya a rundunar ‘yan sandan Najeriya ta jihar Imo, ta tabbatar wa BBC labarin kisan gillar da ‘yan bindigar suka yi wa shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Ideato ta Arewa a jihar, mai suna Chris Ohizu, ƙasa da kwana biyu da sace shi.

Majiyar ‘yan sandan ta ce, rundunarsu tana ƙoƙarin ceto shugaban ƙaramar hukumar daga hannun ‘yan bindigan da suka sace shi, sai kwatsam a daren Lahadi aka yi aune da wasu hotunan bidiyo da ke nuna yadda aka durƙusar da shi kan gwiwoyinsa, a wani ƙungurmin daji, aka ɗaure masa hannaye a harɗe ta baya, daga bisani kuma aka sare masa kai.

Amma dai rundunar ‘yan sandan ta bayar da tabbacin tana ci gaba da gudanar da bincike, har sai ta zaƙulo waɗanda ake zargi da tafka wannan aika-aika.

A ɗaya daga cikin hotunan bidiyon da suka karaɗe shafukan sada zumunta, da ‘yan bindigan suka saki, an ji wata murya tana barazanar halaka shi kansa gwamnan jihar ta Imo, Hope Uzodimma nan ba da daɗewa ba.

Muryar ta kuma ce, su ba ‘yan kungiyar tsaro ta ESN ko kungiyar ‘yan a-waren Biafra ta IPOB ba ne. Su dai gungun wasu mutane ne da ke fafutukar tabbatar da kafuwar jamhuriyyar Biafra a yankin kudu maso gabashin Najeriya, inda suka lashi takobin ba za su bari a gudanar da babban zaben da ke tafe ba.

Ko da a ranar Juma’ar da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga suka sace shugaban ƙaramar hukumar na riƙo, bayan sun harbe shi da bindiga a kafa, sannan suka banka wa gidansa wuta.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto dai gwamnatin jihar Imo ba ta ce uffa ba, game da aukuwar wannan lamari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp