Dakarun Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar ‘yan bindiga a jihar Kaduna

Dakarun sojojin Najeriya rukuni na huɗu da wasu dakaru na musamman na bataliya ta 167 sun kashe ‘yan bindiga tare da ceto mutane 14 da aka yi garkuwa da su a Jihar Kaduna.

Dakarun waɗanda suka shafe dogon lokaci suna bata kashi da ‘yan bindigar a yankin Ƙaramar Hukumar Chikun sun tashi wata maɓoyar ‘yan bindigar a lokacin rikicin.

Wannan na Cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida Samuel Aruwan ya fitar, inda yace “yayin wannan samame an ceto mutane 14, da suka hadar  da maza tara da mata biyar. An kai waɗanda aka ceto ɗin wani wuri mai aminci za a yi musu gwaje-gwaje kafin a haɗa su da iyalansu.”

A cewarsa a yayin wannan simamen, dakarun sun lalata sansanin ‘yan bindiyar da dama an kuma kwato wasu motoci biyu.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 12 hours 3 minutes 14 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 44 minutes 39 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com