• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Taska Zambar N2.2bn: EFCC ta Sake Gurfanar da ɗan Tsohon Shugaban PDP
  • Taska

Zambar N2.2bn: EFCC ta Sake Gurfanar da ɗan Tsohon Shugaban PDP

By
Prnigeria
-
March 25, 2023
Court
Arewa Award

Zambar N2.2bn: EFCC ta Sake Gurfanar da ɗan Tsohon Shugaban PDP

 

Hukumar da ke Yaƙi da yi wa Tattalin Arzikin Najeriya Zagon ƙasa EFCC ta sake gurfanar da Mamman Ali, ɗa ga tsohon shugaban jam’iyyar PDP na ƙasar Ahmadu Ali, bisa zargin zambar naira biliyan 2.2 na tallafin man fetur.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN, ya ruwaito cewa an sake gurfanar da Mamman Ali tare da wani mutum mai suna Christian Taylor da kamfanin mai na Nasaman Oil Services Ltd. a gaban wata kotu a birnin Legas.

An gurfanar da su ne bisa zarge-zagen laifuka 49 ciki har da haɗa baki, da yaudara da zamba cikin aminci, da yin ƙarya domin karɓar kuɗi da amfani da takardun bogi.

To sai dai mutanen sun musanta duka zarge-zargen da ake yi musu.

Lauyan hukumar EFCC Samuel Atteh, ya nemi kotun da ta sanya ranar sauraron ƙarar ta yadda zai gabatar da shaidunsa da za su tabbatar da zargin da hukumar ke yi wa mutanen.

Read Also:

  • Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC
  • DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X
  • Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-

To sai dai lauyan waɗanda ake zargin Kolade Obafemi ya nemi kotun da ta bayar da belin waɗanda yake karewa.

To amma lauyan EFCC ya ce abu mafi muhimmaci kan wannan shari’a shi ne waɗanda ake zargi su riƙa halartar kotun don fuskantar tuhumar da ake yi musu.

Daga ƙarshe alƙalin kotun ya bayar da umarnin cewa waɗanda ake zargin su ci gaba da kasancewa a hannaun hukumar EFCC har zuwa lokacin da za a gabatar da takardun neman belinsu a hukumance.

Alƙalin ya kuma ɗage sauraron ƙarar har zuwa ranar 30 ga watan Mayu mai zuwa.

A ɗaya daga cikin zarge-zargen da hukumar EFCC ke yi wa mutanen, shi ne zargin haɗa baki don karɓar naira miliyan 750 daga gwamnatin tarayya, don karyar bai wa kamfanin mai na Nasaman Oil Services Ltd, ƙarƙashin asusun tallafa wa kamfanonin mai don shigo da litar mai 10,031,986, da kamfanin na Nasaman Oil Services Ltd, ya yi iƙirarin cewa ya saya daga kamfanin man Birtaniya na SEATAC Petroleum Ltd.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • efcc
  • PDP
Previous articleMagance Karancin Naira: CBN ya Umarci Bankuna da su yi Aiki a Ranakun Asabar da Lahadi
Next articleAdamawa: Ayyana Zaɓen Gwamna a Matsayin Wanda bai Kammala ba shi ne Daidai – Binani
Prnigeria

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Azumin Bara: Talge Muka Riƙa Sha a Hannun Maharan Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna

Magance Karancin Naira: CBN ya Umarci Bankuna da su yi Aiki a Ranakun Asabar da Lahadi

Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

Hukumar NITDA ta Gabatar da Satifiket ga Matan da Suka Samu Horo Kan Fasahar Zamani

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

An Gudanar Da Bikin Arewa Stars 30 Under 30 2022, Cikin Nasara

Manomi Yayiwa Wata Mata Yankan Rago

‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

Gidauniyar Malam Inuwa Da Kokarinta Na Ilmantar Da Mutanen Karkara Da Rugage

Gidauniyar Malam Inuwa ta Ɗauki Nauyin Koyar da Ƴa’yan Fulani Al-ƙur’ani

Bincike: Shin Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) ta ƙirƙiro da Tambayoyi Domin Tantance kungiyoyin Musulmi da Kirista a kidayar 2023? 

An Cire Mukaddashin Babban Akantan Najeriya, Mr Chukwuyere Anamekwe

Recent Posts

  • Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC
  • DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X
  • Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-
  • Gwamnan Kano ya tarɓi masu zanga-zangar ƙin kalaman Lawan Triumph
  • Gwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jini

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1571 days 23 hours 12 minutes 57 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1554 days 54 minutes 22 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu - INECDSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin 'aibata' Tinubu a shafin XGwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-Gwamnan Kano ya tarɓi masu zanga-zangar ƙin kalaman Lawan TriumphGwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jiniƳan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan KatsinaRundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami'anta a Jihar BenueNasarar da Daliban Kano suka Samu a NECO kokarin Ganduje ne - Sanusi KiruWata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami'an KAROTA umarniSojojin Najeriya sun cafke kwamandan IPOBƳanbindiga sun hallaka mutum 22 a Jamhuriyyar NijarSojojin Nijeriya sun hallaka mayakan boko haram 5 a jihohin Borno da TarabaNDLEA ta kama Ba'indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a LegasLikitoci a Najeriya sun janye yajin aikin gargaɗiKotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15
X whatsapp