ECOWAS ta sake yin kiran a murkushe ta’addancin da ke karuwa a tsakiyar Sahel

Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS) ta jaddada buƙatar a ɗauki matakan gaggawa domin magance ƙaruwar hare-haren ta’addanci a tsakiyar Sahel.

Kwamishinan ECOWAS da ke kula da harkokin siyasa da zaman lafiya da tsaro, Ambasada AbdelFateh Moussa ne ya yi wannan kira a wani taron bayar da horo na yini biyar.

An yi wa taron taken Tabbatar da ci gaban zaman lafiya: Rawar ƴan sanda da jami’an Jandarma wajen tafiyar da ayyukan ECOWAS wajen wanzar da zaman lafiya.

ECOWAS ce ta shirya taron haɗin gwiwa da kwalejin horas da ƙananan jami’an soji ta Najeriya tare da tallafin shirin ECOWAS kan zaman lafiya da tsaro.

Moussa ya ce ayyukan wanzar da zaman lafiya da aka saba na zama tsohon yayi saboda yanayin rikici a yankin.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 22 hours 22 minutes 55 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1173 days 4 minutes 20 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com