Home SIYASA Kotu ta ce masu ƙalubalantar nasarar Tinubu su biya miliyan goma-goma

Kotu ta ce masu ƙalubalantar nasarar Tinubu su biya miliyan goma-goma

Babbar kotun tarayya da ke Abuja baban birnin Najeriya ta yi watsi da ƙarar da wasu mazauna birnin suka shigar a gabanta suna neman ta hana rantsar da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu.

Yayin da yake yanke hukuncin ranar Talata, alƙalin kotun, Mai shari’a Inyang Ekwo, ya umarci masu ƙarar da kowannensu ya biya naira miliyan 10 ga ministan shari’a kuma Atoni janar na ƙasar.

Masu ƙarar dai na iƙirarin cewa shugaban ƙasar Bola Tinubu bai samu kashi 25 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa a baban birnin tarayyar Abuja, dan haka suke ganin bai cancanci zama shugaban ƙasar ba.

Mai shari’a Ekwo ya ce masu karar ba su da ‘yancin shigar da ƙarar a kotun, yana mai cewa a gaban kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe ne kawai ya kamata a shigar da ƙasar, a maimakon babbar kotun tarayyar da ke Abuja.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp