Home General Ma’aikatan Nijeriya zasu rabauta da horon Tattara bayanai

Ma’aikatan Nijeriya zasu rabauta da horon Tattara bayanai

Gwamnatin tarayyar kasar Nijeriya ta kaddamar da wani shiri na horas da ma’aikatanta dubu 10 hanyoyin tattara bayanai na zamani domin gudanar da ayyukan su cikin tsari.

Hukumar dake lura da bayanai ta kasar nan wato Nigeria Data Protection Commission da hadin gwiwar Data.org ne suka shirya gudanar da shirin, domin horas da ma’aikatan gwamnatin tarayyar kasar nan abinda dokar tattara bayyanai ta shekarar 2023 ta kunsa domin sanya su a turbar data dace wajen gudanar da ayyukan su.

Ministan yada labarai, kirkire-kirkire da tattalin arziki na zamani, Dr. Bosun Tijjani yace hadin gwiwa tsakanin hukumar ta NDPC da Data.org kamar wani somin tabi ne cikin a yunkurin hukumar na daidaita ayyukan ma’aikatan Gwamnatin tarayya tare da inganta musu shi da ilimi da dabaru.

Wadanda zasu rabauta da wannan horo dai sun hadar da shuwagabanin bayanai, manyan dakarun tattara bayanan tsaro, da kuma da kuma masu lura da tattara bayanai gami da masu kula da tsaron na’ura mai kwakwalwa wanda ke aiki a ma’aikatun gwamnatin tarayya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp