Home DUNIYA Mali ta sake dakatar da kafar talabijin mallakin Faransa TV5 Monde

Mali ta sake dakatar da kafar talabijin mallakin Faransa TV5 Monde

Gwamnatin Sojin Mali ta dakatar da yaɗa shirye-shiryen gidan talabijin na TV5 a ƙasar har na tsawon watanni 3 bayan zargin tashar da yaɗa labaran rashin adalci a shirye-shiryenta sakamakon fitar da bayanai ba tare da jin dukkanin ɓangarorin da labarin ya shafa ba.

Tashar ta TV5 mai yaɗa shirye-shiryenta da harshen faransanci ita da kanta da sanar da wannan hukunci na mahukuntan na Mali ga kamfanin dillancin labarai na AFP.

Sanarwar da Sojin na Mali suka fitar sun ce hukuncin zai fara aiki nan ta ke wato daga jiya 11 ga watan Stumban da muke ciki.

Hukumomin na sojin na Mali sun zargin wannan tashar da bada labarai da suka sabawa dokokin ƙasar.

Da samun wannan labari, kungiyoyi kare hakokin ƴan jarida ta kasa da kasa wato RSF da babbar murya ta na mai bayyana damuwa da kuma takaici ganin ta yada hukumomin sojin Mali suka aiwatar da wannan mataki ba tare da tuntuba ba.

Matakin shi ne na dakatar da watsa shirye-shiryen wannan tasha na tsawon watanni uku bisa zargin su da rashin daidaito a fannin yada labarai biyo bayan farmaki dakarun kasar a yankin Tinzaoutaene.

Hukumar Kula da Sadarwa ta kasar ta Mali (HAC) ta soki tashar ta TV5 Monde da bayar da rahoto a ranar 25 ga Agusta, a cikin labarun ta na Afirka, mutuwar akalla fararen hula goma sha biyar a harin da jirage marasa matuka a Tinzaouatène da ke arewacin kasar ta Mali.

Tashar ta TV5  a cikin wata sanarwa ta na mai nadama da kuma nuna mamakin ta na ganin hukumar kula da sadarwa ta kasar ta Mali ba ta nemi jin ko ta bakin masu wakiltar wannan tashar ba kafin daukar irin wannan mataki .

Ko a ƴan shekarun da suka gabata, ƴan lokuta bayan juyin mulkin sojojin kasar an dakatar da kafofin watsa labarai da yawa da kafafan yada labarai na France24 da kuma Radio France Internationale (RFI).

Haka zalika Sojin na Mali sun kuma dakatar da France2 a farkon shekarar 2024, kafin LCI ta fuskanci irin wannan makoma a karshen watan Agusta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp