Mayaƙan Boko Haram sun ƙaddamar da farmaki kan sansanin sojin Najeriya da ke Ƙaramar Hukumar Marte a jihar Borno, inda suka kashe wani adadi na sojojin da ba a bayyana ba.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da harin wanda aka kai da misalin karfe 3 na safiyar wannan Litinin kan sansanin sojin na Forward Operation mai ɗauke da bataliya ta 153 kamar yadda jaridar Daily Trust da ake wallafawa a Najeriyar ta rawaito.
Read Also:
Ɗaya daga cikin majiyoyin da ya buƙaci sakaya sunansa ya shaida wa manema labarai cewa, mayaƙan na Boko Haram sun kuma yi garkuwa da wasu sojojin na Najeriya bayan sun raba su da muhallansu a yayin farmakin.
ISWAP ta karɓe iko da Marte, sun kashe wani adadi na sojoji, sun kuma yi garkuwa da wasu, wasu da dama sun tsere zuwa Dikwa, kuma yanzu haka suna samun mafaka a sansanin runduna ta 24 da ke Dikwa
Ƴanta’addar sun kona tankunan yaƙi tare da awon gaba da tarin makamai daga sansanin sojin a cewar majiyar tsaron.
Ƙaramar Hukumar Marte dai, na da tazarar kilomita 38 daga Ƙaramar Hukumar Dikwa a jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin Najeriya
Wata majiya a Dikwa ta shaida wa Daily Trust cewa, an jiyo ƙarar harbe- harbe
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 4 hours 5 minutes 50 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 5 hours 47 minutes 15 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com