Home SIYASA Shugaba Buhari ya ta ya Tinubu Murnar Cika Shekaru 70 da Haihuwa

Shugaba Buhari ya ta ya Tinubu Murnar Cika Shekaru 70 da Haihuwa

Shugaba Buhari ya ta ya Tinubu Murnar Cika Shekaru 70 da Haihuwa

 

Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, jigon jam’iyyar APC kuma dan takarar shugaban kasa a zaben 2023, zai cika shekaru 70 a ranar Talata, 29 ga Maris.

Gabanin bikin zagayowar ranar haihuwarsa, shugaba Buhari Buhari ya fitar da sanarwar taya murna ga tsohon gwamnan jihar Legas.

Shugaban ya jinjinawa jajircewa, juriya, rashin nuna son kai da martabar Tinubu wajen fifita jin dadin al’umma da hadin kan al’umma sama da son rai.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bi sahun ‘ya’yan APC da shuwagabanninta wajen taya jagoran jam’iyyar na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Legas, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu murnar cika shekaru 70 da haihuwa a ranar 29 ga Maris, 2022.

Shugaban kasar, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin ta hannun mai magana da yawunsa, Femi Adesina, ya tabbatar da irin gudunmawar da jigon na APC ke bayarwa ga ci gaban siyasa, tattalin arziki da zamantakewar kasar nan.

Daily Trust ta rahoto cewa, Buhari ya kuma yaba da jajircewarsa, juriyarsa, rashin nuna son kai da martabarsa a ko da yaushe yana fifita hadin kan al’umma sama da son kai.

Hakazalika, tare da samun goyon baya da hangen nesan Najeriya mai girma ta hanyar zuba jari ga mutane, hukumomi da gwamnatoci, ba tare da tunanin kabilanci ko akida ba.

Ya kuma yi addu’ar Allah ya karawa Asiwaju Tinubu, Jagaban Masarautar Borgu karfi da lafiya da hikima domin ya ci gaba da yi wa kasa hidima da kuma bil’adama baki daya.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp