Home SIYASA SIYASA: Kwankwaso Yayi Murabus

SIYASA: Kwankwaso Yayi Murabus

Kwamishinan Ma’aikatar Raya karkara ta Jihar Kano Dr Musa Iliyasu Kwankwaso ya ajiye mukamin sa na Kwamishina, sa’oi bayan gwamnan jihar ya bukaci hakan ga masu muradin tsayawa Takara cikin jami’an gwamnatin.

Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso yace ya ajiye mukamin nasa ne domin yana da sha’awar yin takarar Dan Majalisar wakilai dake wakiltar Kananan Hukumomin Kura, Madobi da Garun Mallam a zauren majalisar wakilai a zabe mai zuwa, kamar yadda guda cikin hadiman sa Musa Dan Zariya ya shaidawa PRNigeria Hausa ta wayar tarho.

Tsohon Kwamishinan yace “Ina fatan Zan Zama Dan takarar Majalisar wakilai da zai wakilci Kananan Hukumomin Kura Madobi da Garun Mallam a jam’iyyar APC.

Tuni kwamishinan Ruwa na Jihar Kano Sadiq Wali yayi murabus daga kujerar sa, inda ya sayi Fom din takarar Gwaman jihar Kano a Jam’iyyar PDP.

Idan za’a iya tunawa a safiyar lahadi wani rahoto ya bayyana yadda gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje na bada Umarni ga Masu rike da mukamai a gwamnatin Kano dasu ajiye mukamansu Matukar suna da sha’awar tsayawa takara a zabe Mai Zuwa.

Umarnin daya yi dadai da sashe na 84 (12) na sabuwar dokar zabe da aka yiwa gyaran fuska.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp