Home SIYASA Gwamnonin Arewacin Nijeriyar sun yi Fatali Da Zabin Lawan Matsayin Dan Takarar...

Gwamnonin Arewacin Nijeriyar sun yi Fatali Da Zabin Lawan Matsayin Dan Takarar APC

Ta cikin wata ganawa da sukayi da shugaban kasa muhammadu Buhari, Gwamnonin, sun jaddada aniyar sun a mayar da mulkin Kudancin kasar a shekarar 2023

Shugaban kungiyar Gwamnonin kuma gwamnan jihar Plateau Simon lalong, ne ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ganawar a fadar shugana kasa dake Villa a babban birnin tarayyar Nijeriya, inda yace shugaba Buhari ya tabbatar musu cewa bai goyi bayan wani mutum ba cikin mutum 23 da ke son jam’iyyar ta tsayar da su Takara.

Shi ma da yake jawabi, shugaban kungiyar gwamnonin APC kuma gwamnan Jihar Kebbi, Atiku Bagudu, ya ce sun dauki matakin goyon bayan dan takara daga kudancin kasar ne domin tabbatar da adalci da zaman lafiya a kasar.

Dambarwar da ake yi kan batun dan takarar shugaban kasar na Najeriya a jam’iyyar APC ta sa shugaban kasar Muhammadu Buhari ya fitar da sanarwa yana nesanta kansa ga goya wa kowanne dan takara baya.

Wannan kuma na kunshe ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Malam Garba Shehu ya aike wa manema labarai inda ya ambato Shugaba Buhari yana cewa babu wanda ya zaba a matsayin dan takarar APC na shugaban kasa a zaben 2023.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp