Home SIYASA Daga Karshe, Atiku ya Zaɓi Okowa a Matsayin Abokin Tafiyarsa

Daga Karshe, Atiku ya Zaɓi Okowa a Matsayin Abokin Tafiyarsa

Okowa and Atiku

Daga Karshe, Atiku ya Zaɓi Okowa a Matsayin Abokin Tafiyarsa

 

‘Dan takarar shugabancin kasa karkashin inuwar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bayyana Gwamna Ifeanyi Okowa matsayin abokin tafiyarsa.

Duk da kwamitin shawari ta zabi Gwamna Wike na jihar Ribas, an gano cewa Atiku ya sakankance cewa Wike bayan kaunarsa.

Har ila yau, wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP, ba su aminta da Gwamna Wike ba ganin irin kusancin da kujerar take da ta shugaban kasa.

FCT, Abuja – Atiku Abubakar, ‘dan takarar shugabancin kasa karkashin jam’iyyar PDP, ya zabi Ifeanyi Okowa, gwamnan jihar Delta a matsayin abokin tafiyarsa a zaben 2023 mai gabatowa.

Kwamitin gudanar da ayyuka na jam’iyyar PDP a ranar Laraba ya zabi Nyesom Wike, gwamnan jihar Ribas, a matsayin wanda zai kasance mataimakin ‘dan takarar shugabancin kasan.

Mambobin NWC sun yi zabe inda Wike ya samu kuri’u 13 yayin da Okowa ya samu uku kacal, lamarin da yasa masu ruwa da tsakin suka aminta da Wike.

Sai dai, Atiku Abubkar na gano ya kasa sakin jiki da Wike a matsayin abokin tafiyarsa sabodaya sakankance cewa gwamnan baya kaunarsa.

Wike yayi wa Aminu Waziri Tambuwal aiki a zaben fidda gwani na 2019, duk da kuwa cewa Atiku ya zo ya lashe zaben, Arise Tv ta ruwaito.

Wasu manya a PDP an gano ba su aminta da Wike ba saboda tsananin kusancin mataimakin shugaban kasa da kujerar shugabancin kasan.

Ya sanar da zabinsa ne a ranar Alhamis a hedkwatar jam’iyyar PDP ta lasa dake Abuja. Ya ce ya yanke wannan shawarar ne bayan dogon nazari da tattaunawa da masu ruwa da tsakin jam’iyyar.

A cewarsa, hukunci ne mai tsauri gare shi wurin yankewa duba da irin nagartattun mutanen da aka shawarcesa ya zaba daga ciki. “Ina farin cikin sanar da sunan Gwamna Ifeanyi Okowa a matsayin mataimakin ‘dan takarar shugaban kasa.

Ina hango tafiyar da kasar mu, tare da dukkan ‘yan Najeriya da kuma gina zaman lafiya, hadin kai da cigaba ga kowa,” ya wallafa a shafinsa na Twitter.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp