Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina ta Fatattaki ‘Yan Ta’addan tare da ceto...

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina ta Fatattaki ‘Yan Ta’addan tare da ceto Mutane 18 da aka yi Garkuwa da su

Rundunar ‘yan sandan jihar katsina tace ta sami nasarar fatattakar ‘yan bindiga a yayin da suka farwa kauyukan Baushe da Gatakawa dake karamar hukumar Kankara a jihar.

wannan na kushe ta cikin wata sanarwa da aka raba ga manema labarai da kakakin hukumar SP Gambo Isah ya fitar a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar.

sanarwar tace ‘yan ta’addan masu tarin yawa bisa babura dauke da bindigu kirar AK 47, sun tasamma kauyukan inda suke harbi kan mai uwa da wabi, nan jami’an ‘yan sanda suka kai dauki bayan samun rahotanni bisa jagograncin baturen ‘yan sanda na kankara.

rundunar ta yi nasarar fatattakar ‘yan ta’addan daga kokaringudanar da mummunan harin da suka yi niya tare da kubutar da dukkannin wadanda aka yi garkuwa da su. inda  suka sami nasarar kwato babura biyar da shanu biyu.

sai dai sanarwa ta bayyana ewa ‘yan bindigar sun halaka mutum biyu mazauna kauyen baya ga raunata mutum guda. ko da yake ana kallon an hallaka ‘yan bindigar da dama kko kuma sun tsere da raunikan harbi a jikkunansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp