Home Labarai Gwamnatin Buhari na shirin cire tallafin Man Fetur

Gwamnatin Buhari na shirin cire tallafin Man Fetur

Gwamnatin Najeriya ta ce ta na shirin kammala cire tallafin man fetur kafin mika mulki ga sabuwar gwamnati a ranar 29 ga watan Mayun wannan shekara.

Ministar kudi da tsare tsaren kasar Zainab Shamsuna Ahmed ta bayyana shirin a Abuja, inda ta ke cewa shirin cire tallafin shi ne wanda jama’a basa so amma kuma ya zama wajibi, a dai dai lokacin da akasarin ‘yan Najeriya suka yarda cewar tallafin baya taimakon talaka.

Ahmed ta ce sun samu umurnin cire tallafin nan da watan Yuni na wannan shekara kamar yadda majalisa ta amince da shi a cikin kasafin kudin wannan shekara, kuma za su aiwatar da shi domin bai wa kasuwa damar samar da farashin a koda yaushe.

Ministar ta ce idan an cire tallafin, zai ba iwa ‘yan kasuwa da masu zuba jari damar shiga harkokin kasuwancin man da kuma samar da shi ga jama’a.

Zainab Ahmed ta ce kawo karshen zuba tallafin man zai bai wa gwamnati damar karkata kudin da ake sanyawa zuwa bangarori da dama da suka hada da inganta asibitoci da makarantu da kuma samar da kayan more rayuwa.

Ministar ta bukaci ‘yan Najeriya da su goyawa gwamnatin baya wajen ganin an kawo karshen wannan tallafi wanda ke amfana wasu mutane ‘yan kadan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp