Home General Shugaban NLC zai bayyana a gaban ƴan sanda

Shugaban NLC zai bayyana a gaban ƴan sanda

A yau ne Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago, Joe Ajaero zai amsa gayyatar ƴan sanda domin amsa wasu tambayoyi game da zarginsa da ɗaukar nauyin ta’addanci da laifukan kafofin sadarwa da cin amanar ƙasa da sauransu.

Ƴan sanda dai sun gayyaci shi ne bayan wani samame da suka kai a sakatariyar NLC da ke Abuja.

“Ƴan sandan sun ce sun yi samamen ne domin gano wasu muhimman abubuwa da suke da alaƙa da zanga-zangar matsin rayuwa da aka yi a Najeriya,”

Domin nuna goyon baya ga Ajaero, Ƙungiyar Ƙwadago ta umarci mambobinta a faɗin ƙasar da su taru a hedkwatar ƴan sanda na jihohinsu, “har sai shugabansu ya bar hedkwatar ƴan sandan.”

Idan ba a manta ba, dubban mutane ne suka fito suka yi zanga-zangar matsin rayuwa, ƙarƙashin jagorancin wata ƙungiya mai suna Coalition of Concerned Nigerian Citizens.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp