Home AFIRKA DalilinTanzania na dakatar da jaridar The Citizen a kasar

DalilinTanzania na dakatar da jaridar The Citizen a kasar

Gwamnatin Tanzania ta dakatar da wata jarida da ke kan gaba a ƙasar da ake wallafawa a shafin internet, bayan ta wallafa hotunan da ke alakanta shugabar ƙasar, Samia Suluhu Hassan da sace-sace da kuma kashe kashen ƴan adawa da aka yi a baya-bayan nan.

Ɗaya daga cikin hotunan bidiyo da jaridar The Citizen ta wallafa  ya nuna shugaba Samia Suluhu Hassan zaune tana kallon bidiyon cin zarafin da aka yi wa ƴan adawa haɗe da wasu da ba su ji ba basu gani ba.

Gabanin faruwar lamarin shugabar ƙasar ta fuskanci caccaka daga ciki da wajen Tanzania game da zarge-zargen da ake yi wa jami’an tsaron ƙasar da alhakin yin garkuwa tare da kashe wasu daga cikin jiga jigan jamiyyar adawa na ƙasar.

Tuni dai jaridar ta cire tallace-tallacen da ta wallafa, kana ta fitar da sanarwar da ke cewa manufarsu ita ce bayyana damuwar allummar ƙasar a game da matsalolin tsaro.

A ranar Laraba ne The Citizen da ke kan gaba daga cikin jaridun da ake walafawa da harshen Turanci a Tanzania ta fitar da sanarwar dakatar da ayyukanta na tsawon kwanaki 30 da hukumar da ke kula da harkokin sadarwa ta  Tanzaniya ta yi.

Tun a cikin watan Agustan da ya gabata ne dai, gwamnatin Samia Suluhu Hassan ta haramta manyan gangami biyu da jam’iyyar Chadema ta ƙaddamar, sannan ta sanar da batun tsare shugabannin jam’iyyar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp